Home Labarai Zaben 2023: NNPP Ta Ci Zabe Ta Hanyar Magudi A Kano – Ado Doguwa

Zaben 2023: NNPP Ta Ci Zabe Ta Hanyar Magudi A Kano – Ado Doguwa

by Muhsin Tasiu Yau

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai kuma dan majalisa mai wakiltar mazabar Tudun Wada/Doguwa na Jihar Kano, Alhassan Ado Doguwa, ya yi ikirarin cewa jam’iyyar NNPP mai mulki a jihar ta lashe zaben 2023 ta hanyar magudi.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa jam’iyyar NNPP ta samu rinjayen kuri’u a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairun 2023 da kuma kujeru masu rinjaye a zabukan ‘yan majalisar dokokin jihar da aka gudanar a rana guda.

Daga nan ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta ayyana jam’iyyar a matsayin wadda ta lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

Related Posts

Leave a Comment