Home Labarai Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ƙaddamar Da Tallafi Ga Manyan Limamai, Masu Kiran Sallah

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Ƙaddamar Da Tallafi Ga Manyan Limamai, Masu Kiran Sallah

by Muhsin Tasiu Yau

Gwamnatin jihar Katsina Ta Ƙaddamar Da Tallafi Ga Manyan Limamai, Masu Kiran Sallah

Gwamnatin jihar Katsina ta samar da alawus-alawus na musamman ga daukacin manyan Limamai na masallatan Juma’a da mataimakansu da masu kiran Sallah a fadin jihar.

Gwamna Dikko Umaru Radda  ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da kwamitin kula da harkokin tsaro na kananan hukumomi talatin da hudu na jihar wanda ya gudana a gidan gwamnatin jihar.

Gwamna Umaru Radda ya ce an dauki matakin ne domin zaburar da malaman addinin su hada kai wajen yaki da rashin tsaro.

Related Posts

Leave a Comment