Home Labarai ‘Yan Sanda Sun cigaba da tuhumar Matar da ta kashe Mijinta a Bauchi

‘Yan Sanda Sun cigaba da tuhumar Matar da ta kashe Mijinta a Bauchi

by masta

Matar da ta kashé mijinta a Bauchi sunanta
Maimunatu Sulaiman ‘yar Shekara 21, sunan mijinta Aliyu Muhammad

Kamar yadda ta bayyana wa ‘yan sanda masu bincike, tace cacar baki ne ya shiga tsakaninta da mijinta, sai da ta bari sun kwanta a kan gadonsu na Sunnah da nufin zasuyi bacci bayan kammala cacar bakin, sai ta dauko wuka ta caka masa a kirjinsa wanda hakan yayi ajalinsa

Yanzu haka tana nan a sashin binciken manyan laifuka na ‘yan sanda State CID Bauchi, idan an kammala hada bincike za’a gurfanar da ita a Kotu

Related Posts

Leave a Comment