Daga shafin jaridar Alfijir

Ƴan Sanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 5, Sun ƙwato Shanu 143 A Katsina
Alfijir Labarai ta rawaito Rundunar ‘yan sandan Katsina ta ce an kashe wasu da ake zargin ‘yan fashi ne guda biyar a wasu hare-hare da suka kai a maboyar bata gari a jihar.
A wata sanarwa da kakakin rundunar, Abubakar Aliyu ya fitar ranar Lahadi, ya ce jami’an hukumar yaki da garkuwa da mutane da na hukumar bincike ta musamman (SIB), tare da hadin gwiwar mafarauta da ’yan banga ne suka hada kai.
Ya kara da cewa an kai wasu hare-hare a sansanonin ‘yan bindiga a kauyukan Marake, Garin Yara da Garin Labo a karamar hukumar Batsari.
Karamar Hukumar Jibia ta kuma dauki bakuncin wasu ‘yan samame tare da “sansanin wani Audu Lankai, wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga” da aka kaiwa hari.
Aliyu ya ce an kama Abubakar Idris dan shekara 18, wanda ake zargin dan fashi ne kuma an kwato dabbobi 143 a samamen.
“Kwamandan rundunar da ke kula da sashin yaki da garkuwa da mutane da kuma na hukumar bincike ta musamman (SIB) ne ya jagoranci wannan samamen,” in ji shi.
Hakazalika tawagar ta yi nasarar fatattakar wasu sansanonin ‘yan bindiga da dama a kauyukan Marake, Garin Yara da Garin Labo, duk a karamar hukumar Batsari.
“Rundunar ta kuma tarwatsa wani sansanin wani Audu Lankai, shugaban ‘yan bindiga da ke addabar Jibia da kewaye.”
Aliyu ya bayyana cewa an kwato shanu 38, tumaki 40 da awaki 65 a sansanonin da aka kai farmakin.
Ya ce har yanzu ‘yan sandan na ci gaba da binciken inda lamarin ya Ƴan Sanda Sun Kashe Ƴan Bindiga 5, Sun ƙwato Shanu 143 A Katsina.

