Home Labarai Dillalan Albasa 11 Ne Suka Mutu, Sama Da 50 Kuma Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota

Dillalan Albasa 11 Ne Suka Mutu, Sama Da 50 Kuma Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota

by Muhsin Tasiu Yau

Akalla ’yan kasuwa 11 da ke kai albasa da sauran amfanin gona daga karamar hukumar Goronyo ta Jihar Sakkwato zuwa Jihar Neja ne aka tabbatar da mutuwarsu a wani hadari.

Lamarin wanda ya afku a ranar Litinin din da ta gabata a kan hanyar Maiyama/Koko a karamar hukumar Koko-Besse ta jihar Kebbi, hadarin ya raunata wasu fasinjoji kusan 50, wadanda a halin yanzu suke samun kulawa a asibiti.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubabar, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Related Posts

Leave a Comment