Home Labarai Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

Shari’ar kotunan Nijeriya ta zama tufka da warwara – PDP

by Muhsin Tasiu Yau

Wasu masana shari’a a Nijeriya sun soki shari’o’in na Kano, Zamfara, da Filato. Daga cikinsu akwai ƙwararren lauya Femi Falana, wanda ya nemi a sake duba hukuncin.

Kazalika, rundunar ‘yan sanda a jihar Kano ta yi gargaɗin hukunta “masu shirin shirya zanga-zanga bayan samun wasu bayanai da ke nuna cewa wasu qungiyoyin magoya bayan jam’iyyu na yunƙurin shiryawa domin nuna ɓacin rai kan hukuncin kotun”.

A ranar Juma’ar da ta gabata ne kotun ɗaukaka ƙara a Abuja ta bai wa Nasir Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC nasara a zaɓen gwamnan jihar Kano, inda ta soke nasarar gwamna mai ci Abba Kabir Yusuf na jam’iyyar NNPP.

Hukuncin kotun ya ce Abba bai cancanci zama ɗan takarar gwamna ba, saboda shi ba ɗan jam’iyya ba ne.

Related Posts

Leave a Comment