392
A karshe dai kotun kolin ta sanya ranar Alhamis 26 ga watan Oktoba domin yanke hukunci na karshe a kararraki biyu da suka rage na kalubalantar halascin ko akasin haka na ayyana shugaba Bola Tinubu a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa da ya gabata.
Wannan wani koke ne da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, da takwaransa na jam’iyyar Labour, LP, LP, Peter Gregory Obi suka shigar.
Daraktan yada labarai na kotun koli, Dr Aemeri Festus Akande, ya tabbatar da hakan a ranar Laraba.
Ya ce an samar da isassun tsaro domin dakile tabarbarewar tsaro a ciki da wajen harabar kotun.

