Maiɗakin Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Aisha Buhari. Ta ce “Yanzu babu sauran zuwa ƙasar waje duba lafiyar wani shugaban Nijeriya…”
Haj. Aishatu Buhari ta bayyana haka ne cike da karsashi, a lokacin da ake duba asibitin fadar shugaban ƙasa dake Villa, wanda ta ce ya laƙumi maƙudan kuɗi masu yawa da ake daf da kammala shi.
Sai dai a lokacin da maiɗakin shugabam ƙasar take wannan bayani, ana cikin kwana na biyu da fara yajin Likitoci a ƙasar nan.
Asibitin fadar gwamnatin Nijeriyar da a yanzu a ke daf da kammala shi, ana ganin idan har aka kammala shi, to zai kawo ƙarshen tafiya ƙasar waje ga duk wani shugaban ƙasa, ko muƙarrabansa don a duba lafiyar su.
Abin jira a gani dai a yanzu shi ne, shin samar da asibitin zai kawo ƙarshen fitar shuwagabannin ƙasar nan zuwa asibitocin ƙasar wajen don a duba lafiyarsu?
Daga: Nafiu Salisu


