Home Labarai Gwamnatin Dikko Radda za ta shirya wa dukkanin Farinsifal na makarantun sakandaren gwamnatin jihar Katsina da mataimakansu jarabawar cancantar rike wadannan mukaman

Gwamnatin Dikko Radda za ta shirya wa dukkanin Farinsifal na makarantun sakandaren gwamnatin jihar Katsina da mataimakansu jarabawar cancantar rike wadannan mukaman

by masta

Duk wanda bai ci jarabawar ba zai iya rasa nukaminsa ya koma rike alli

Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare ta jihar Katsina a ranar Talata ta sanar da cewa, ana shirin gudanar da jarabawar gwaji ga ɗaukacin shugabanni (Principals) mataimakan shugabannin makarantun sakandire da ke fadin jihar.

Sakamakon jarabawar aka yi a cewar kwamishinan ma’aikatar Hon. Zainab Musawa, zai taimaka wajen naɗa mukamai tare da tabbatar da bin cancanta a makarantu, ta yadda za a inganta kwazo da ingantaccen jagoranci a makarantun.

Hakanan Kwamishiniyar ta karyata rahotannin da kafafen yada labarai suka yada a baya-bayan nan da ke nuna yadda jihar ta samu sakamakon jarabawar NECO ta shekarar 2024

A cewarta, duk da yawan adadin da aka samu, jihar Katsina ta samu matsayi na shida a fadin kasar nan a cikin adadin daliban da suka ci jarrabawar NECO da maki biyar da sama da haka, wadanda suka hada da Mathematics da Ingilishi, inda dalibai 29,633 suka samu wannan muhimmin matsayi.

Related Posts

Leave a Comment